Harkar Fasa Kwabri Ta Karu Bayan Rufe Iyakokin Najeriya

A kasuwar Limbe dake kudu maso yammacin Kamaru, masu saye da sayarwa na cikin gida da na Najeriya sun ce tun bayan da gwamnatin Najeriya ta rufe bakin iyakokin ta, kasuwancin su ya fuskanci koma baya.

Yan kasuwar sun ce suna yawan samun karancin kayayyaki daga kasashen biyu, abinda ya janyo hauhawar farashen kayayyaki da kashe 15 cikin 100.

Wata matashiya ‘yar shekara 35 da haihuwa mai suna Miracle Ademola, na saida riguna a Kamaru daga nan kuma sai ta sayo shinkafa don ta saida a Najeriya. Ademola ta koka akan makudan kudaden shiga da fitar da kayayyaki ta jirgin ruwa da ake sanyawa.
Hukumar kididdigar Kamaru ta ce kusan ‘yan kasar ta 15,000 ne ke kasuwanci a tsallaken iyakar Najeriya.

Hakazalika su ma ‘yan Najeriya suna zuwa Kamaru sarin kayan gona, ciki har da shinkafa, albasa, auduga da ma shanu don ‘yan kasuwar su.
‘Yan sanda da jami’an kwastam a kudu maso yammacin garin Buea dake Kamaru sun kona wasu magunguna masu yawan gaske da aka yi fasa kwabrin su daga Najeriya ranar Lahadin da ta gabata.

Masu sukar lamiri sun ce rufe iyakokin Najeriya ya kawo shakku akan yarjejeniyar cinikayya ba tare da wani shinge a nahiyar Afrika da aka cimma a watan Yulin shekarar 2018.

Amma hukumomi a Najeriya na jaddada cewa har yanzu kofofin kasuwancin kasar na nan bude ta tashoshin jiragen ruwa.

More News

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban RiÆ™on Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...