Hadakar Kungiyoyin Kudancin Najeriya Na Kira Ga Fulani

Hadakar kungiyoyin Yarbawa, yankin Naija Delta, da ta jama’ar tsakiyar Najeriya ta Afenifere, da ta Kudancin kasar sun maida martani.

Kungiyoyin sun maida martani ne game da kiran da wata kungiyar Dattawan Arewacin Najeriya tayi cewa, Fulani makiyaya dake zaune a yankin kudancin kasar su dawo Arewa.

Sanarwar wanda shugabannin kungiyoyin irin su Cif Ayo Adebanjo na afenefere dana Chaneze Ndigbo Cif Nnia Nwodo, da Edwin Clark na Naija Delta, suka rattabawa hannun, sunyi Allah wadai da kiran da kungiyar Dattawan Arewa karkashin jagorancin Farfesa Ango Abdullahi tayi na Fulani su koma yankin Arewa domin rayukan su na cikin hatsari.

Koda yake wakilin Muryar Amurka bai samu jin tabakin shugabannin na Afenefere game da wannan sanarwa ba, sarakunan Yarbawa sunyi kira ga Fuani dake wannan yanki da suyi watsi da kiran na barin yankin, su kuma cigaba da gudanar da kiwon dabbobin su, domin tabbatar da zaman lafiya, kamar yadda daya daga cikin sarakunan yarbawa maimartaba Oba Ahmed Adekunle Oyelude ya shaida.

Domin jin tabakin sauran al’ummar yanki dana Arewa, wasu sun ce cece kuce tsakanin kungiyoyin yankin na Arewacin Najeriya da kuma takwarorinsu na Kudanci ko Yanmancin kasar, ya fito ne bayan wani matakin gwamnatin Muhammadu Buhari tace, zata kafa Rugage a yankunan kasar ciki harda Kudu.

Koda yake daga baya ta soke shirin, gwamnati ta fitar da sanarwar ta hannun kakakin fadar shugaban kasa, Malam Garba Shehu inda tayi kira ga Fulanin dake zaune a kudancin Najeriya da suyi watsi da wannan kira da shugaban kungiyar Dattawan Arewacin kasar, farfesa Ango Abdullahi yayi.

Suma ‘yan jam’iyar APC mai mulki a Legas sunyi tsokaci akan wannan al’amarin, kamar yadda daya daga cikin shugaba Alhaji Ado Dansudu yayi bayani.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...