Habasha: Abiy Ahmed ya lashe zabe | Labarai

Firaminstan Habasha Abiy Ahmed ya lashe zaben ‘yan majalisun dokokin da aka gudanar a kasar da gagrumin rinjaye kamar yadda hukumar zaben kasar mai zaman kanta ta bayyana.
Hukumar zaben ta ce Aby Ahmed ya samu kujeru 421 daga cikin 436 na kujerun ‘yan majlisun kasar, lamarin da ka sake bashi wata dama na ci gaba da tafiyar da mulkin Habasha.
Sai dai zaben na 12 ga watan Yuni, ya fuskanci wasu tarin kalubalai na tsaro a yankunan kasar da dama, musamman yankin Tigrey inda a ya zo daidai lokacin da ake fafatwa tsakanin ‘yan tawayen yankin da dakarun gwamnati, kafin cimma matsaya kan tsagaita wuta a karshen watan Yuni.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]