Haɗarin mota ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 14 a Kigo

Mutane 14 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 13 suka samu raunuka daban-daban a wani hatsarin da ya faru a unguwar Aloma da ke karamar hukumar Ofu a jihar Kogi.

Hatsarin da ya afku a ranar Lahadin da ta gabata ya hada da wata motar bas kirar Toyota Sienna da ta nufi Abuja daga Fatakwal da wata motar bas kirar Toyota Hiace da ta nufi Kudancin kasar.

Shaidun gani da ido sun ce hatsarin ya afku ne a lokacin da wasu motocin kirar Toyota guda biyu na kasuwanci suka yi karo da juna.

Wani ganau ya ce, “Mutane 13 da suka hada da direban Hiace Bus gaba daya gobarar ta kone.

Amma daya daga cikin mutane hudu da suka tsira a cikin motar bas din sun mutu a asibiti saboda konewar da suka samu wanda ya kawo adadin zuwa 14 da suka mutu.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]