A ranar Lahadin ne wani mummunan hatsarin kwale-kwale a karamar hukumar Mokwa da ke jihar Neja ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 24.
Gwamnan jihar Neja Mohammed Bago ya bayyana matukar kaduwarsa da faruwar lamarin kuma tun a lokacin ya yi kira da a dauki matakan kare lafiya cikin gaggawa.
Hadarin ya afku ne tsakanin karfe 7:30 na safe zuwa karfe 8:00 na safe a al’ummomin da ke tsakanin Jebba da madatsar ruwan Kainji. Yawancin wadanda abin ya shafa mata ne da kananan yara.
Sama da mutane 30 ne aka ceto ya zuwa yanzu, sakamakon hadin gwiwar jami’an ‘yan sandan ruwa, masu ruwa da tsaki, da hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Neja.
Gwamna Bago, a cikin wata sanarwa ta hannun babban sakataren yada labaransa, Bologi Ibrahim, ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa.