Gwamnonin arewa za su zabi sabon shugaban a wurin taron da suka fara a Kaduna

Gwamnoni dake halartar taron ya yin da suka halarci sallar Juma’a

A ranar Juma’a ne gwamnonin arewa 19 za su zabi sabon shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa biyo bayan karewar wa’adin shugaban kungiyar, gwamnan jihar Borno Kashim Shettima.

Gwamnan jihar ta Borno da ya yiwa gwamnonin jawabi ya yin taron dake gudana gidan gwamnatin jihar Kaduna ya shawarci gwamnonin da suka halarci wurin taron da su goyi bayan duk wanda ya samu nasarar zama sabon shugaban kungiyar.

Shettima ya kuma nemi gafara daga abokan aikinsa idan har ya saba musu a lokacin da yake gudanar da aikinsa.

Shugaban mai barin gado ya lissafa nasarori da dama da kungiyar ta samu karkashin jagorancinsa inda ya shawarci shugaban da zai maye gurbinsa da ya kai kungiyar ya zasu mataki na gaba.

Duk da cewa shugaban bai bayyana yadda za a zabi sabon shugaban ya shawarci abokan aikinsa da su goyi bayan duk wanda aka zaba.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...