Gwamnonin APC sun ziyarci Tinubu

A ranar Juma’a ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya yi wata ganawar sirri da gwamnonin jam’iyyar All Progressives Congress, APC.

Shugaba Tinubu a wani sako da ya wallafa a Facebook ya tabbatar da ganawar da gwamnonin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

“A yau na ji dadin tarbar fitattun Gwamnoni daga babbar jam’iyyar mu ta APC zuwa fadar gwamnati.

“Mun sake jaddada aniyarmu da kuma kokarin hada kanmu wajen ganin mun cimma kyawawan manufofinmu ga Nijeriya. Idanuka hada ƙarfi da karfe, za mu nasara wajen neman kasa mai wadata.” Ya buga

Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ne ya jagoranci gwamnonin zuwa fadar gwamnatin, wanda kwanan nan ya karbi mukamin shugaban kungiyar Progressives Governors’ Forum, PGF.

Gwamnonin APC 17 daga cikin ashirin ne suka halarci taron.

Wadanda suka halarci taron sun hada da Gwamna Oluwarotimi Akeredolu na jihar Ondo da Abiodun Abayomi Oyebanji na jihar Ekiti da kuma Dr Nasir Idris na jihar Kebbi da sauransu.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...