Gwamnonin APC sun ziyarci Tinubu

A ranar Juma’a ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya yi wata ganawar sirri da gwamnonin jam’iyyar All Progressives Congress, APC.

Shugaba Tinubu a wani sako da ya wallafa a Facebook ya tabbatar da ganawar da gwamnonin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

“A yau na ji dadin tarbar fitattun Gwamnoni daga babbar jam’iyyar mu ta APC zuwa fadar gwamnati.

“Mun sake jaddada aniyarmu da kuma kokarin hada kanmu wajen ganin mun cimma kyawawan manufofinmu ga Nijeriya. Idanuka hada ƙarfi da karfe, za mu nasara wajen neman kasa mai wadata.” Ya buga

Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ne ya jagoranci gwamnonin zuwa fadar gwamnatin, wanda kwanan nan ya karbi mukamin shugaban kungiyar Progressives Governors’ Forum, PGF.

Gwamnonin APC 17 daga cikin ashirin ne suka halarci taron.

Wadanda suka halarci taron sun hada da Gwamna Oluwarotimi Akeredolu na jihar Ondo da Abiodun Abayomi Oyebanji na jihar Ekiti da kuma Dr Nasir Idris na jihar Kebbi da sauransu.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...