Gwamnatin Zamfara za ta bayar da tallafi saboda rage raɗaɗin matsin tattalin arziki

Gwamnatin jihar Zamfara ta bada izinin raba kayan abinci cikin gaggawa ga daukacin kananan hukumomin 14 a wani mataki na rage tasirin cire tallafin man fetur.

Matakin a cewar mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya nuna irin sadaukarwar da gwamnati mai ci ta yi na rage radadin kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta.

Bala ya ce, “Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da a gaggauta raba kayan abinci a matsayin abin da zai rage wahalhalun da aka samu kai a ciko sakamakon cire tallafin man fetur.

“Kashin farko na rabon abinci zai fara ne da Shinkafa, Masara da sauransu.”

More from this stream

Recomended