Majalisar zartaswar jihar Zamfara ta amince da daukar mambobi 4200 aiki a rundunar hadin guiwa ta Civilian Task Force (JTF) don taimaka wa kokarin da hukumomin tsaro ke yi na magance matsalar rashin tsaro a yankin.
Ma’aikatan na daga cikin muhimman batutuwan da aka tattauna a taron SEC da Gwamna Dauda Lawal ya jagoranta, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris ya fitar ranar Talata.
Taron ya kuma amince da gina sabbin ajujuwa, gyare-gyare da kuma kayyade kayayyakin makarantun a wani bangare na kudirin gwamnati na kara samun damar karatu.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A kokarinsa na dakile matsalar rashin tsaro, Gwamna Dauda Lawal ya amince da daukar ma’aikatan civilian JTF a daukacin kananan hukumomin jihar.
“Yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwar jihar, Gwamnan ya kuma amince da gina sabbin ajujuwa, gyare-gyare da kuma samar da kayayyakin da ake da su a fadin kananan hukumomi 14 na jihar.”