Gwamnatin Zamfara ta yi gagarumin yunƙuri don magance matsalolin tsaro

Majalisar zartaswar jihar Zamfara ta amince da daukar mambobi 4200 aiki a rundunar hadin guiwa ta Civilian Task Force (JTF) don taimaka wa kokarin da hukumomin tsaro ke yi na magance matsalar rashin tsaro a yankin.

Ma’aikatan na daga cikin muhimman batutuwan da aka tattauna a taron SEC da Gwamna Dauda Lawal ya jagoranta, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris ya fitar ranar Talata.

Taron ya kuma amince da gina sabbin ajujuwa, gyare-gyare da kuma kayyade kayayyakin makarantun a wani bangare na kudirin gwamnati na kara samun damar karatu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A kokarinsa na dakile matsalar rashin tsaro, Gwamna Dauda Lawal ya amince da daukar ma’aikatan civilian JTF a daukacin kananan hukumomin jihar.

“Yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwar jihar, Gwamnan ya kuma amince da gina sabbin ajujuwa, gyare-gyare da kuma samar da kayayyakin da ake da su a fadin kananan hukumomi 14 na jihar.”

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]