Gwamnatin Jihar Lagos, karkashin Akinwumi Ambode, ta fara rushe gine-ginen da suka nuna alamar za su iya ruguzowa a yankin itafaji dake Lagos Island.
Yanzu haka jami’an gwamnati na can a layin Freeman dake yankin Ita Faji suna gudanar da aikin rusaun.
Rushe gine-ginen na zuwa ne kwanaki biyu bayan da wani ginin bene mai hawa uku dake layin Massey ya rufta.
Ginin da ya rufta na dauke da makarantar firamare a hawa na biyu
Mutane 12 ciki har kananan yara 9 ne suka mutu a lamarin ya yin da aka samu nasarar ceto mutane sama da 50.
Ruftawar gini abun da yake yawan faruwa a Najeriya kuma hukumomin sun gaza shawo kan faruwar lamarin.