A jiya ne dai aka tashi da rahotonnin cewa kasar na yunkurin rufe 80 daga cikin ofisoshin jakadancinta fadin duniya.
Rahotannin sun ce za ta rufe su ne saboda ba ta da halin ci gaba da gudanar da su. an kuma ce kasafin kudin baya-bayan nan ya ware kudin da za a gudanar da ayyukan ofisoshi talatin ne kawai.
To sai dai wani jami’an gwamnatin kasar ya ce rahoton ba shi da wani tushe ballanatana makama.
A ranar Laraba ne dai kwamitin harkokin kasashen waje na majalisar dattawan kasar ya bayyana cewa ofisohin jakadancin kasar a fadin duniya na cikin wani mummunan yanayi, inda kuma kwamitin ya zargi gwamnatin tarayyar kasar da yin watsi da su.