Gwamnan jihar Kano,Engr Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da shirin raba fom ɗin jarrabawar UTME ga ɗaliban sakandaren jihar dubu 6500.
A wata sanarwa gwamnan ya ce ya yi hakan ne domin samar da damarmaki ga É—aliban jihar na halartar makarantun da suke gaba da sakandare.
“A Æ™oÆ™arin mu na samar da damarmaki na cigaba da karatun gaba da sakandare ga Æ´an asalin jihar Kano na Æ™addamar da rabon fom É—in jarrabawar JAMB UTME guda 6500 ga É—aliban makarantun sakandare,” ya ce.
Ya ce gwamnatinsa ta samu cimma manyan nasarori a bangaren bunÆ™asa ilimi a jihar a cikin watanni goman da suka gabata da suka haÉ—a da dawo da shirin tura Æ´an asalin jihar Æ™aro karatu a jami’o’in Æ™asashen waje, biyan kuÉ—in makaranta na É—aliban jihar dake manyan makarantu da sake buÉ—e makarantu 21 na koyon sana’a.