Gwamnatin Kano Ta Musunta Rusa Makarantar Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara


Sabanin yadda wasu kafofin labarai a Najeriya suka wallafa rahotanni, rushe -rushen bai shafi makaranta mallakar Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara ba, mutumin da gwamnatin jihar Kano ta yiwa daurin talala a gidan sa tun daga ranar Alhamis din nan.
Sai dai majiyoyi daga unguwar sun tabbara da cewa, shehin malamin na amfani da wani bangare na filin da gine-gine basu kai gareshi ba wajen gudanar da wa’azin sa a lokuta daban-daban.
A nata bangare, hukumar raya birane ta jihar Kano ta musanta cewa ta rusa makarantar Sheikh AbdulJabbar Nasiru Kabara, a cewar kakakin hukumar Ado Mohammed Gama.
Tun a shekara 2002 ne gwamnatin jihar Kano ta yanka fulotai a filin wadda gabanin haka tsohuwar makabarta ce da ake bunne mutane.
Bayan samar da Fulotan gwamnati ta mallaka su ga wasu daga cikin mazauna unguwar ta Gwale da sauran makwafta. Amma a wancan lokaci mutane ba su fara ginawa ba saboda tsoron tuno gawawwaki.
Malam Rabiu Gwale dake zaman sakataren kungiyar ci gaban Gwale ya ce wadanda aka mallakawa fulotan sun fara gine-gine a karshen shekara 2020, wato bara kenan.
Sai dai a cikin watan jiya na Janairu ma’aikatar ilimi ta ce, zatayi amfani da filin domin gina makaranta saboda ta gano wata wasika da wasu mutane suka aika mata tun shekarun baya suna muradin a gina makarantar a wurin, saboda gwamnatin Kano ta soke fulotan data tsara a wurin tun a shekara ta 2012, kamar yadda kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Muhammad Sanusi Kiru ke cewa.
To amma sakataren kungiyar ci gaban Unguwar ta Gwale Malam Rabiu ya ce ba san da wannan magana ba, yana mai cewa, kafin su fara gine-ginen su sai da suka sanar da ma’aikatar dake kula da taswirar bini da kewayen Kano wadda itace ta fitar musu da taswirar yadda gine-gine a wurin zasu kasance, tare da bada lambar fuloti ga mutane da aka baiwa.
A don haka sai Malam Rabiu, ya ce suna rokon gwamnati ta ja hankalin ma’aikatar ilimi game da wannan batu, la’akari da cewa, galibin fulotan da gine-ginen da aka fara mallakar Marayu ne a yanzu.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...