Gwamnatin Borno Ta Wanke Wasu Mutane 500 Da Ake Zargin Su Da Hannu A Ayyukan Ta’addanci

Gwamnatin jihar Borno ta wanke wasu mutane  daga zargin da ake masu na hannu a ayyukan ta’addanci a jihar.

Kafin a wanke mutane daga dukkanin zargin da ake masu ana tsare da su ne a barikin sojoji ta Giwa dake Maiduguri.

Kamfanin Dilalancin Labaran Najeriya NAN ya rawaito cewa kwamishiniyar mata ta jihar Borno,Zuwaira Gambo ita ta sanar da haka a ranar Laraba da take jawabi ga wasu  mata da suka gudanar da zanga-zanga.

Hajja Gana wacce ke jagorantar matan ta yi zargin cewa sojoji suna cigaba da tsare yaransu da basu aikata laifin komai ba.

Gambo ta ce an saki waɗanda ake zargin rukuni rukuni inda aka miƙawa gwamnatin jihar Borno su.

“Rukunin Æ™arshe  sune mutane 28 da aka saka makon da ya wuce,” ta ce.

Gambo ta tabbatarwa da waɗanda ƴan uwansu suke tsare a hannun sojoji kan rikicin Boko Haram da kada suji tsoro matuƙar sun tabbatar da cewa basu aikata laifin komai ba.

Kwamishiniyar ta ce gwamnati na aiki kafaÉ—a da kafaÉ—a da sojoji domin ta tabbatar da cewa anyi adalci ga kowa.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...