Gwamnan Yobe ya ziyarci wuraren da ambaliyar ruwa ya shafa

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya kai ziyara wasu sassan jihar da ambaliyar ruwa tayi mummunan barna.

A yayin ziyarar gwamnan ya jajantawa al’ummar garin Jumbam inda aka rasa rayukan mutane 10 a wani hatsarin jirgin ruwa.

Garuruwan Jumbam da Kaliyari dukkansu a karamar hukumar Tarmuwa na daga cikin inda ambaliyar ruwan tayi wa mummunan barna.

Har ila yau gwamnan ya bayar da umarnin gaggauta sake gina titunan da ambaliyar ruwan ta lalata.

More from this stream

Recomended