Gwamnan Sokoto ya fara ba da alawus wa mutane masu nakasa

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya fara biyan alawus-alawus na N6,500 duk wata ga masu fama da nakasa a jihar.

Sakataren yada labarai na gwamnan, Malam Abubakar Bawa, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, inda ya kara da cewa an fara biyan kudaden ne a ranar Talata a cibiyoyi uku na kananan hukumomin Sokoto ta Arewa, Dange Shuni da Gwadabawa na jihar.

Ya ce shirin ya samu tarin mutanen da aka riga aka tantance, wadanda suka karbi Naira 6,500 kowanne a matsayin alawus din su na wata-wata.

Sanarwar ta ruwaito wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin sun yaba wa gwamnan kan maido da alawus alawus din na wata.

Sun ce hakan zai bi su wajen inganta rayuwarsu, baya ga rage barace-barace a kan tituna.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...