Gwamnonin PDP za su gudanar da taro ranar Talata kan halin da kasa ke ciki

Gwamnonin jam’iyar PDP za su gudanar da wata ganawa ranar Talata domin tattauna halin da al’amura ke gudana a Najeriya.

A cikin wata sanarwa ranar Litinin dake sanar da taron, Cyril Maduabum darakta janar na kungiyar gwamnonin jam’iyar PDP ya ce za kuma a tattauna halin da jam’iyar take ciki.

Maduabum ya ce taron wanda shi ne karo na farko tun bayan gwamnan Bauchi, Bala Muhammad ya karbi ragamar jagorancin kungiyar gwamnonin za a gudanar da shi a masaukin baki na gwamnatin Akwa Ibom dake Abuja.

“Ana sa ran kungiyar za ta tattauna kan halin da kasa ke ciki musamman abubuwan dake faruwa a yan kwanakin nan ta bangaren siyasa, zamantakewa da kuma tattalin arziki,” a cewar sanarwar.

More from this stream

Recomended