Gwamnan jihar Ondo Rotimi Akeredolu ya mutu

Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu ya mutu.

Jaridar Punch ta rawaito cewa Akeredolu ya mutu ne da safiyar ranar Laraba yana da shekaru 67. An rawaito cewa gwamnan ya mutu sanadiyar cutar sankarar mafitsara da kuma ta jini.

Wasu majiyoyi a gidan gwamnatin jihar sun tabbatarwa da jaridar The Cable mutuwar gwamnan.

A ranar 7 ga watan Satumba ne gwamnan ya dawo daga jinyar tsawon watanni uku a kasar Jamus inda ya mayar da ofishinsa birnin Ibadan na jihar Oyo

Rashin mika mulki ga mataimakinsa ya haifar da rikicin siyasa a jihar har ta kai ga majalisar dokokin jihar tayi barazanar tsige mataimakin gwamnan jihar, Lucky Aiyedetiwa.

Biyo bayan tsoma bakin shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu majalisar dokokin jihar ta janye batun tsige mataimakin gwamnan kana shima mataimakin gwamnan ya janye karar da ya shigar gaban kotu domin ta hana majalisar dokokin jihar tsige shi.

A ranar 12 ga watan Disamba ne gwamnan ya sanar da cewa zai sake tafiya hutun jinya kuma ya mika ragamar jagorancin jihar ga mataimakin gwamnan jihar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...