Gwamnan jihar Niger, Umar Bago ya yi afuwa ga fursunoni 80 dake gidajen gyaran hali daban-daban a jihar.
Sakataren gwamnatin jihar, Abubakar Usman ya ce yin afuwa ga daurarrun na daga cikin wani bangare na bikin Ranar Dimakwaradiyya ta 2023.
Usman ya ce gwamnan ya kuma bayar da umarnin a gaggauta biyan tarar da aka yi wa fursunoni kamar yadda kwamitin shawara na jihar kan yiwa fursunoni afuwa ya bayar.
Ya yi kira ga fursunoni da su guji yin abin da zai sake mayar da su gidan yari.