Gwamnan Jigawa zai biya wa asalin ƴan jihar kuɗin makaranta

Gwamna Umar Namadi ya amince da biyan kudin rijistar ɗaliban Jhar Jigawa wadanda suke karatun digiri daban-daban a Jami’ar Tarayya, Dutse FUD, Jami’ar Bayero, Kano (BUK), Jami’ar Fasaha ta Jihar Kano (KUST) da Jami’ar Maiduguri.

Kuɗin da aka ware ya kai dadin naira miliyan ɗari da sittin da bakwai da dubu ashirin da hudu da ɗari tara da hamsin (N167,024,950.00).

Matakin Majalisar Zartarwar Jihar ya yi dai-dai da tsarin gudanarwa na yanzu don taimaka wa iyaye masu karamin karfi su shawo kan karuwar kudaden makaranta ga ‘ya’yansu.

Hakazalika majalisar ta amince da sake duba tallafin karatu ga ‘yan asalin jihar Jigawa nan take kuma lokacin da za a biya kudaden ya kasance a farkon kowace shekarar makaranta.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...