Gwamnan Jigawa zai biya wa asalin ƴan jihar kuɗin makaranta

Gwamna Umar Namadi ya amince da biyan kudin rijistar ɗaliban Jhar Jigawa wadanda suke karatun digiri daban-daban a Jami’ar Tarayya, Dutse FUD, Jami’ar Bayero, Kano (BUK), Jami’ar Fasaha ta Jihar Kano (KUST) da Jami’ar Maiduguri.

Kuɗin da aka ware ya kai dadin naira miliyan ɗari da sittin da bakwai da dubu ashirin da hudu da ɗari tara da hamsin (N167,024,950.00).

Matakin Majalisar Zartarwar Jihar ya yi dai-dai da tsarin gudanarwa na yanzu don taimaka wa iyaye masu karamin karfi su shawo kan karuwar kudaden makaranta ga ‘ya’yansu.

Hakazalika majalisar ta amince da sake duba tallafin karatu ga ‘yan asalin jihar Jigawa nan take kuma lokacin da za a biya kudaden ya kasance a farkon kowace shekarar makaranta.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama ƴan kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan ƴan sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan ƴan...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...