Gwamnan Bauchi ya bada umarnin ɗaukar ma’aikata 1480

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya amince a ɗauki sabbin ma’aikata 1480 domin cike gurbin da hana ɗaukar ma’aikata da gwamnatin, Barrister Muhammad Abubakar ta saka ya haifar.

Gwamnan Abubakar ya dakatar da daukar ma’aikata domin ya samu damar tantance su domin a cewarsa suna cinye kaso mai tsoka na kuɗin da jihar take samu shima Bala Muhammad ya cigaba da bin wannan tsari a lokacin da yake kokarin raba jihar da ma’aikatan bogi a mulkinsa zango na farko

Biyo bayan rantsar da shi a karo na biyu, Muhammad ya sanar da janye hanin domin cika alkawarin da ya ɗauka ga mutanen jihar a ranar 29 ga watan Mayu.

Shugaban ma’aikatan jihar, Adamu Yahuza shi ne ya sanar da haka ga yan jarida a jiya.

Ya ce 1000 daga cikin ma’aikatan da za a ɗauka za su kasance malaman makaranta.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]