Gwamna Ahmad Aliyu Ya Kaddamar da Shirin Tallafa Wa Karatun Yara Mata a Sokoto

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, ya kaddamar da wani shiri na musamman don tallafa wa karatun yara mata a duk faɗin jihar, a wani yunƙuri na rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Shirin, wanda aka yi wa take da “Adolescent Girls’ Initiative for Learning and Empowerment” (AGILE), na nufin inganta damar da mata yara za su samu na ilimi, tare da ƙarfafa ayyukan koyo da koyarwa a jihar Sokoto.

A cikin wani saƙo da gwamnan ya wallafa a shafin Facebook ɗinsa, ya bayyana cewa, ƙarƙashin wannan shiri, makarantun sakandare na mata guda 240 za su amfana da tallafin kuɗaɗe domin inganta ilimi a tsakanin su.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]