Majalisar sojoji da ke mulkin Sudan da babbar kungiyar fararen hula masu zanga-zanga a kasar sun cimma yarjejeniya kan sabon wa’adin gwamnatin rikon kwarya da za a kafa a kasar.
Kasar Sudan na cikin rikicin siyasa tun bayan da sojoji suka hambare tshon Shugaba Omar al-Bashir a watan Afrilu.
Jakadan Kungiyar Kasashen Afirka, AU, Mohamed Hassan Lebatt ne ya sanar da cima yarjejeniyar da sanyin safiyar yau Asabar amma bai bayar da cikakken bayani ba.
Mista Lebatt ya bayyana wa manema labarai cewa: “Ina sanar da ‘yan kasar Sudan da ‘yan Afirka da sauran mutanen duniya cewa wakilan bangarorin biyu sun amince da yarjejeniyar a hukumance.”
Ya kuma ce akwai sauran aiki da za a yi kafin a fayyace sauran abubuwa, gabanin rattaba hannu kan daftarin yarjejeniyar, amma bai bayar da cikakken bayani ba.
An dai shafe watanni ana tattaunawa tsakanin gwamnatin mulkin soji ta kasar da kungiyoyin fararen hula a daidai lokacin da tashin hankali ke neman jefa kasar cikin yakin basasa.
A watannin baya, gwamnatin ta Sudan da masu adawa da ita sun cimma yarjejeniya kan batutuwa masu yawa, amma da zarar an kusa rattaba hannu kan yarjeniyoyin, sai wani bangare ya fito da wasu sabbin bukatu.
Daftarin yarjejeniyar da aka amince da shi a watan jiya ya fayyace cewa za kafa wata sabuwar gwamnati da fararen hula shida da janar-janar na sojojin kasar biyar.
- Sudan na neman kara rincabewa
- Ana gudanar da sabuwar zaga-zanga a Sudan
Me daftarin yarjejeniyar ya kunsa?
Tuni dai aka cimma wata matsaya game da raba mukamai tsakanin bangarorin biyu, kuma bangarorin sun amince da yawancin mataka da aka bayyana.
Na farko shi ne za a gudanar da mulkin karba karba na wata 39, kafin a gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar kasar.
Za a nada firai minista wanda bangare masu zanga-zanga ne za su nada, kuma shi ne zai jagoranci majalisar ministocin kasar.
Amma sojoji ne za su nada ministan tsaro da na harkokin cikin gida.