Gobe Tinubu zai cilla Netherlands don gudanar da ziyarar aiki

A ranar Talata 23 ga watan Afrilun 2024 ne shugaban kasa Bola Tinubu zai bar Abuja zuwa kasar Netherlands domin ziyarar aiki.

Shugaban kasar zai kuma halarci taron tattalin arzikin duniya da aka shirya gudanarwa a ranakun 28 zuwa 29 ga watan Afrilu a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Litinin, ya ce, “Bisa goron gayyatar da firaministan kasar Netherlands, Mark Rutte, ya yi masa, shugaba Tinubu zai tattauna da firaministan kasar, tare da yin shawarwari masu zurfi da tarurruka daban-daban tare da Mai Martaba Sarki Willem-Alexander da Sarauniya Maxima ta Masarautar.

“Sarauniyar ita ce mai ba da shawara ta musamman ga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, watau UNSGSA.

Shugaban zai samu rakiyar wasu ministoci da wasu manyan jami’ai.  jami’an gwamnati.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...