‘Gobara ta lalata dukiyar naira tiriliyan uku a Najeriya’

Gobara ta lalata dukiyar da ta kai ta naira biliyan dubu 3, wato tiriliyan 3 a Najeriya, kamar yadda Ministan harkokijn cikin gida na kasar, Rauf Aregbesola ya bayyana.

Ministan ya ce kasar ta tafka wannan asara ne a sanadiyyar gobara 2,845 da aka samu a sassan kasar daban-daban a shekarar da ta wuce, 2021.

Aregbesola

Aregbesola ya sanar da haka ne jiya Laraba yayin da yake sanya lambobin karin girma ga manyan shugabannin hukumar kashe gobara ta tarayyar kasar, a Abuja.

Ministan ya kuma ce hukumar ‘yan kwana-kwana ta yi nasarar kare kadarar da ta kai ta naira tiriliyan 18.9 trillion da ceto mutane 260 daga gobara.

Ministan, wanda ya ce hukumar ta samu kiran gaggawa tare da kai dauki na kashe gobara har 2,845 a shekarar da ta wuce 2021, y ace sun samu wannan nasara ne saboda a tsakanin 2015 zuwa yanzu hukumar ta samu kayan aiki fiye da yadda take samu tun lokacin da aka kirkiro ta a 1991.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...