Ganduje Ya Nemi Kotu Ta Hana EFCC Binciken Bidiyon Dala

Tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya nemi wata babbar kotu a jihar da ta hana hukumar EFCC binciken sa har abada akan bidiyon da aka fitar yana saka daloli a aljihun babbar riga.

A shekarar 2018 ne jaridar Daily Nigerian ta wallafa bidiyon da ya nuna Ganduje ya na karɓar cin hancin dala daga wani ɗan kwangila.

A lokacin gwamnan ya ƙaryata bidiyon inda ya ce ƙirƙirar sa aka yi.

Tsohon Antoni Janar na jihar shi ne ya shigar da karar inda ya nemi kotun da ta hana hukumar EFCC binciken sa har sai an kammala shari’ar dake gaban kotu tsakanin Ganduje da Ja’afar Ja’afar mamallakin jaridar ta Daily Nigerian.

Ganduje ta hannun lauyan nasa ya nemi kotun da ta ayyana cewa gayyatowa tare yin tambayoyi ga tsohon shugaban hukumar SUBEB da kuma Akanta Janar na jihar ya saɓa wa ka’ida.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]