Everton ta lallasa Man United

Premier

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Manchester United ta debi kashinta a hannu bayan Everton lallasa ta 4-0 a wasan mako na 35 a Premier da suka fafata ranar Lahadi a Goodison Park.

Everton ta ci kwallo biyu tun kan aje hutun rabin lokaci ta hannun Richarlison de Andrade da kuma Idrissa Gueye.

Bayan da suka koma zagaye na biyu aka kara zura kwallo biyu a ragar United ta hannun Lucas Digne da kuma Theo Walcott.

United, wadda ta buga karawar kamar ‘yan wasanta ba su da lafiya ta samu dama daya kacal da ta buga kwallo ta nufi raga saura minti hutu a tashi daga fafatawar.

Marcus Rashford ne ya samu damar a cikin masu tsaron bayan Evrton, ya kuma buga kwallo ta wuce saman kan mai tsaron raga Jordan Pickford.

Wannan nasarar ta kai Everton zuwa mataki na bakwai a teburin Premier, hakan zai iya kai ta gasar Europa a badi, ita kuwa United ta ci gaba da zama a matakinta na shida.

Sauran maki biyu ne tsakanin United da Arsenal ta biyar a teburi, wadda za ta fafata da Crystal Palace ranar Lahadi.

A ranar Talata ne Barcelona ta fitar da Manchester United daga gasar cin kofin Zakarun Turai ta bana, kuma ba ta kai bantenta a FA Cup ba, kuma Manchester City ce ta lashe Caraboa Cup na shekarar nan.

Everton ta taba cin United 3-0 a gasar Premier ranar Lahadi 26 ga watan Afirilun 2015 a Goodison Park.

Yadda kungiyoyin suka murza-leda.

Hakkin mallakar hoto
BBC Sport

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...