Emefiele: An Samu Yamutsi Tsakanin Jami’an DSS dana Hukumar Gidan Yari

An samu yamutsi a harabar babbar kotun tarayya dake Ikoyi a jihar Lagos bayan da jami’an tsaron DSS suka yi kokarin kwace, Godwin Emefiele tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN daga hannun jami’an hukumar gidan yari ta Najeriya.

A ranar Talata ne aka gurfanar da Emefiele a gaban kotun tun bayan da aka tsare shi a watan Yuni.

Mai shari’a, Nicholas Oweibo ya bayar da belin tsohon gwamnan babban bankin kan kudi naira miliyan 20.

Sauran sharudan sun hada da kawo mutum guda wanda yake da kadara a yankin Ikoyi, mika fasfonsa na tafiye-tafiye da kuma kawo ma’aikacin gwamnati dake matakin albashi na 16.

Alkalin ya yi umarnin a tasa keyar Emefiele zuwa gidan yari har sai ya cika sharudan belin.

Amma mai makon a mika shi ga jami’an gidan yari, jami’an tsaron DSS sun yi kokarin yin gaba da shi yunkurin da ya gamu da turjiya daga jami’an gidan yarin.

A gumurzun da aka yi ta kai ga an yaga rigar wani jami’in gidan yarin.

A karshe dai jami’an na DSS saboda yawansu sun samu nasarar tafiya da Emefiele.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...