Mutanen sun tsere ne daga gidajensu, sanadiyar artabun da dakarun gwamnati ke yi da mayakan masu dauke da makamai, kungiyar likitoci ta kasa da kasa ta MSF ta fada a jiya Talata.
An shiga matsanancin hali na rayuwa a jihar ta Borno cikin shekaru goma da aka kwashe ana rikici da mayakan Boko Haram.
Tun daga watan Disambar bara, an ci gaba da samun karuwar tashe-tashen hankula, lamarin da ya tilastawa dubban mutane tserewa zuwa garuruwan da ke hannun dakarun gwamnati a cewar wata sanarwa da kungiyar ta MSF ta fitar dauke da sa hannun jami’in yada labaranta, Tim Shenk.
“Mutanen da suka tserewa yankin Monguno a kwanan nan, sun fice daga gidajensu inda suka bar komai a baya, yanzu suna kwana ne a kan tituna.” Inji wani jami’in kungiyar ta MSF, Musa Baba.
Kungaiyar likitocin, ta yi kiran samar da wani tsari mai inganci a tsakanin bangaren gwamnatin Najeriya da hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da sauran kungiyoyo masu zaman kansu, domin ganin an tunkari matsalolin da ‘yan gudun hijirar ke fuskanta.