Dattawan Arewa sun nemi Fulani makiyaya su dawo Arewa

Kungiyar Dattawan Arewa ta yi Kira ga Fulani Makiyaya da ke kudancin kasar da su koma Arewa.

A daidai lokacin da jam’iyyar adawa ta PDP ke kira ga Shugaba Muhammadu Buhari da ya kafa dokar ta baci a bangaren tsaro, Kungiyar Dattawan Arewa karkashin jagorancin Farfesa Ango Abdullahi ta yi kira ga dukanin makiyaya da ke kudancin kasar, da su tattara nasu ‘inasu su koma Arewa.

Abdullahi ya yi wannan kira ne inda ya yi ikrarin cewan ba za a ba su kariya ba saboda ka’idar da gwamnonin shiyyar kudancin kasar suka samar wa makiyaya, da ke cewa sai dai su rika diban dabbobinsu a mota amma ba dai su yi kiwo a kasa ba.

Ya ce ya kamata gwamnati ta kafa wani kwamiti mai karfi da zai yi binciken abubuwan da ke faruwa saboda a yi wa kowa adalci idan za a biya diyya bayan sun dawo gida.

Sai dai daya daga cikin shugabannin Gammaiyar Kungiyoyin Matasan Arewa Sherrie Nastura Ashir, ya ce an sha yin irin wadannan tarurukan tun a zamani Marigayi Abacha, amma kuma duk ba su yi wa kasa amfani ba.

Yanzu kiran da suke yi shi ne, a kafa Kwamitin raba gardama, saboda duk wanda yake so ya zauna a Najeriya a ba shi dama ya zauna a duk inda yake so.

A lokacin hada wannana rahoton dai fadar shugaban kasa ba ta ce komai akan wannan lamari ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]