Damisa ta kwanta baccin rana a kan gadon wani magidanci a Indiya

A tiger lying on a bed in Assam state

Damisar ta hau kan gado ta kwanta a cikin wani gida dake jihar Assam

An gano wata macen damisa wacce ta tsere daga wani gandun namun daji a jihar Assam da ambaliyar ruwa ta daidaita a Indiya, kwance a kan gadon wasu mazauna jihar.

Ana tunanin ta gudo ne daga Gandun Namun Daji na Kaziranga inda dabbobi 92 suka mutu a ‘yan kwanakin nan saboda ambaliyar ruwa.

Jami’an wata kungiyar masu fafutukar kare hakkin namun dawa sun isa gidan kuma sun samar wa damisar hanyar fita zuwa daji.

A cewar Gidauniyar Namun Dawa ta Indiya WTI, an fara ganin damisar ne kusa da wani babban titi ranar Alhamis.

Gidauniyar ta ce babu mamaki, kaiwa da komawar da ake yi a kan titin ya matsa mata don haka ta nemi wannan gidan ta shiga, wanda kuma a kusa da babban titin yake.


Mai gidan ya tsere a lokacin da ya tsinkayi damisar

Rathin Barman wanda ya jagoranci cire damisar daga gidan ya ce ta shiga gidan ne da misalin karfe 7 da rabi sannan ta kwanta ta yi ta bacci gaba daya ranar.

“Ta yi matukar gajiya kuma ta samu bacci mai kyau,” a cewarsa.

Sai dai Migidan, Motilal, ya tattara kan iyalinsa kaf a lokacin da ya ga shigowar damisar.

“Abin sha’awa shi ne babu wanda ya matsa mata don ta samu hutawa sosai. Muna matukar girmama namun dawa a wannan yankin,” in ji Mista Barman.

“Molitilal ya ce zai adana zanin gadon da matashin kan da damisar ta hau ta kwanta.”

Jami’an WTI sun tsayar da motoci a kan babban titin tsawon awa guda sannan aka tayar da dabbar daga bacci. Ta tashi sannan ta bar gidan da misalin karfe biyar da rabi na yamma, ta tsallaka titin sannan ta bi hanyar dajin.

Mista Barman ya ce babau tabbacin cewa ta shiga dajin ko kuma da shiga wani wajen ne dake kusa da dajin.

Gandun Namun Daji na Kaziranga na ajiye Damisa 110 amma babu ko daya da ya mutu a ambaliyar ruwan.

Dabbobin da suka mutu a dandun sun hada da barewa 54 da dorinar ruwa 7 da aladen dawa 6 da giwa daya.

Ambaliyar ruwa ta daidaita jihohin gabashin kasar na Bihar da Assam, inda ta kashe sama da mutane 100 da raba miliyoyin mutane da muhallansu.

Lokacin ruwa, wanda ke farawa daga watan Yuni zuwa watan Satumba ya jefa Nepal da Bangladesh cikin rudani.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...