Dan wasan Liverpool dan kasar Senegal Sadio Mane ya bayar da gudunmawar £41,000 ga kwamitin da kasarsa ta nada domin yaki da cutar coronavirus.
Dan wasan ya dauki matakin ne bayan da ya lura da yadda cutar ke yaduwa a kasar ta Senegal.
A wani bidiyo da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Mane ya yi kira a dauki batun yaduwar cutar ta coronavirus da “matukar muhimmanci.”
Dan wasan ya bai wa magoya bayansa shawara kan matakan da za su dauka domi kare kansu daga kamuwa da cutar, kamar “wanke hannu tsawon dakika 30”.
Kawo yanzu, an tabbatar da mutum 27 da suka kamu da Covid-19 a Senegal, ko da yake biyu dsaga cikin su sun warke, a cewar ma’aikatar lafiyar kasar.
Hukumomina Senegal sun sanar da dakatar da sauka da tashin jiragen sama tsakanin kasashen yammaci da arewacin Afrika, da kuma wasu kasashen Turai da dama. (Faransa da Spaniya da Italiya da Belgium da kuma Portugal)
A arewacin Afrika kuwa kasashe kamar Aljeriya da Tuniya yayin da Morocco tuni ta dakatar da saukar jirage daga Senegal din.