Cikin Hotuna: Ziyarar Emmanuel Macron a Nijar

Ranar Lahadi ne Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya kai ziyara kasar Nijar domin yin ta’ziyyar sojojin nan 71 da ‘yan bindiga suka kashe.

Image caption

Shugaba Muhamadou Issoufou na Nijar da twkwaransa na kasar Faransa Emanuel Macron sun kai ziyara makabartar da aka binne sojojin Nijar da ‘yan bindiga suka kashe

Image caption

Macron ya kai ziyarar ne a kan hanyarsa ta zuwa kasar Ivory Coast domin yin bikin Kirsimati tare da sojojin kasarsa

Image caption

Kasar Faransa ce tsohuwar uwar gijiyar Nijar, wadda ta yi wa mulkin mallaka shekara 61 da suka gabata

Image caption

Akwai daruruwan dakarun kasar Faransa a kasar ta Nijar, wadanda suke horarwa tare da taimaka wa wasu rundunonin sojan Nijar din

Image caption

Sai dai ziyarar tasa ta gamu da cecekucen daga wasu ‘yan Nijar, inda suka ce ba sa maraba da shi sannan suka zargi Faransa da mara wa ‘yan bindigar baya

Image caption

Wasu ‘yan kasar ta Nijar, har wa yau, sun yi kiran da Faransa ta tattara komatsanta ta bar masu kasarasu

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]