Cece-Kuce Akan Matsayin Nijar a Zaben Najeriya

Mawakan troupe Albishir, na jamhuriyar Nijar sun rera wakar kamfai ga dan takarar jam’iyyar APC a zaben shugaban kasar da za a gudanar a karshen mako a Najeriya, lamarin da tuni ya haifar da mahawara a yanzu haka a bisa yadda mawakan ke kwatanta wakar a matasyin wata gudunmawa daga shugaban kasar Nijar.

Muryar Amurka ta yi kokarin tuntubar jami’an kasar Nijar, domin jin abin da zasu ce kan wannan Magana, amma hakka bata cimma ruwa ba.

Wannan cece-kuce na faruwa ne kwanaki kalilan bayan da aka hango gwamnan jihar Zinder da na Maradi rataye da tutar APC a wuya a ya yin gangamin jam’iyyar na Kano, abin da ya janyo suka daga jam’iyyar adawa ta PDP wacce ke ganin an yi katsalandan.

Tuni dai kungiyoyi masu zaman kansu suka fara jan hankulan ‘yan Nijar a duk inda suke su nisanci kansu daga dukkan wani yunkurin shiga harakokin zabubukan da za a gudanar a ranar Asabar din da ke tafe a Najeriya don kaucewa fadawa tarkon ‘yan siyasa.

Domin cikakken bayani saurari rahotan Sule Muminu Barma.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...