Buhari zai tafi kasar Ethiopia a ranar Alhamis

Shugaban kasa, Muhammad Buhari ya shirya tsaf domin tafiya kasar Ethiopia inda zai halarci babban taron kungiyar kasashen Afrika ta AU.

A wata sanarwa da fadar shugaban kasa ta fitar ta ce Buhari zai bar Abuja a ranar Alhamis ya zuwa birnin Addis Ababa na Ethiopia.

Buhari zai halarci taron kungiyar AU karo na 36 wanda zai mayar da hankali kan yadda za a gaggauta aiwatar da yarjeniyar kasuwancin bai ɗaya a tsakanin ƙasashen Afrika da a kaiwa lakabi da AFCTA.

Har ila yau a yayin taron ana sa ran shugaban kasa Buhari zai halarci tarukan kungiyar ta AU kan zaman lafiya da tsaro, sauyin yanayi da kuma halin da dimakwardiya ke ciki a wasu ƙasashen Afrika ta yamma.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...