Buhari zai tafi kasar Ethiopia a ranar Alhamis

Shugaban kasa, Muhammad Buhari ya shirya tsaf domin tafiya kasar Ethiopia inda zai halarci babban taron kungiyar kasashen Afrika ta AU.

A wata sanarwa da fadar shugaban kasa ta fitar ta ce Buhari zai bar Abuja a ranar Alhamis ya zuwa birnin Addis Ababa na Ethiopia.

Buhari zai halarci taron kungiyar AU karo na 36 wanda zai mayar da hankali kan yadda za a gaggauta aiwatar da yarjeniyar kasuwancin bai ɗaya a tsakanin ƙasashen Afrika da a kaiwa lakabi da AFCTA.

Har ila yau a yayin taron ana sa ran shugaban kasa Buhari zai halarci tarukan kungiyar ta AU kan zaman lafiya da tsaro, sauyin yanayi da kuma halin da dimakwardiya ke ciki a wasu ƙasashen Afrika ta yamma.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]