[ad_1]
Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Adams Oshiomhole ya bayyana cewa ya yi farin ciki da matakin da wasu ‘yan majalisar tarayya na APC suka dauka na komawa jam’iyyar PDP inda ya bayyana su a matsayin sojojin haya da suka shiga jam’iyyar don cin zabe kawai.
Ya kara da cewa, Shugaba Muhammad Buhari ya fi su karbuwa a Mazabunsu saboda ko a zaben 2015 ya fi samun yawan kuri’u a ainihin mazabun nasu. Oshiomhole ya ce ficewarsu daga jam’iyyar a wannan kako I da zabe ya karato alheri ne saboda hakan zai ba APC damar mayar d hankali kan shirye shiryen zaben 2019.
[ad_2]