Buhari ya fi mazan Najeriya da yawa kwari, inji kungiyar kamfen Buhari

Kungiyar kamfen tazarcen Shugaba Muhammadu Buhari ta ce ‘yan Nijeriya kar su tsorata game da lafiyar shugaban kasar, domin yana cikin koshin lafiya, har ma ya fi da yawan mazajen Nijeriya kwari.

Mataimakin daraktan kungiyar, Arch Waziri Bulama ne ya bayyana hakan yayin da yake tattaunawa da ‘yan jaridu a Abuja.

Bulama ya ce: “Ina ganin yadda Shugaban kasa yake kai-kawo a cikin wannan kamfe din ya nuna cewar ya fi da yawan mazajen kasar nan kwari. Wannan ne mutumin da a shekarunsa yake kai-kawo daga birni zuwa birni, sannan akalla yake zuwa birane biyu a kowacce ranar mako domin kaddamar da ayyuka, haduwa da shuwagabannin gargajiya da masu ruwa da tsaki, sannan kuma ya dawo domin ya fuskanci wasu ayyukan kasa da kuma wasu kungiyoyin a fadarsa ta Aso Rock.

Bayan nan kuma da safiyar washegarin ranar ya kuma shillawa wani garin ba tare da nuna alamar damuwa ko rauni ba. Shugaban kasa Buhari yana da lafiya da matukar kwarin da zai gabatar da ayyukansa, sannan kuma abun alfahari, yana bayar da irin shugabanci da lokacinsa da muke bukata a wannan kamfe din.”

More News

Gwamnatin jihar Kaduna ta kafa kwamitin biyan diyya ga mutanen da harin jirgin sama ya shafa

Gwamnatin jihar Kaduna, ta kafa wani kwamiti da zai biya diyya tare da tallafi ga mutanen da harin jirgin sama marar matuki na rundunar...

Uba Sani ya bayar da umarnin yin bincike kan harin soja da ya kashe mutane 30

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba sani ya bayar da umarnin bincike kan harin jirgin sama da ya kashe mutane da dama a ƙauyen...

APC ta lashe zaɓen dukkanin shugabannin ƙananan hukumomin jihar Ekiti

Jam'iyar APC ta lashe dukkanin zaɓen shugabannin kananan hukumomin jihar Ekiti da kuma na kujerun kansiloli 177 da aka gudanar. A ranar Asabar ne...

APC ta lashe zaɓen dukkanin shugabannin ƙananan hukumomin jihar Ekiti

Jam'iyar APC ta lashe dukkanin zaɓen shugabannin kananan hukumomin jihar Ekiti da kuma na kujerun kansiloli 177 da aka gudanar. A ranar Asabar ne...