Buhari ya bukaci majalisa ta amince da karbo bashin dala miliyan 800

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya roki majalisar dattawa a ranar Laraba da ta amince da lamunin dala miliyan 800 domin gudanar da shirin samar da zaman lafiya a kasar.

Yayin zaman majalisar dattijai na ranar Laraba, Ahmed Lawan, wanda shi ne shugaban majalisar ya karanta wasikar da Buhari ya rubuta mai dauke da bukatar.

Kudaden a cewar shugaban kasar, za a raba wa matsugunan gidaje miliyan 10.2 ne da marasa galihu na tsawon watanni shida, inda aka yi hasashen za su rubanya mutane miliyan 60.

Don ganin an aiwatar da shi yadda ya kamata, shugaban ya bukaci ‘yan majalisar su gaggauta daukar mataki.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]