Boko Haram Ta Yi Yunkurin Kai Hari A Damaturu | VOA Hausa

Wasu da ake zargin ‘yan ta’addan kungiyar Boko Haram sun yi yunkurin kai wani hari a yammacin ranar Lahadi da ta gabata, wanda rundunar sojin Najeriya ta yi nasarar dakile shi.

Wasu mazauna garin Damaturu na jahar Yobe da ke arewa maso gabashin kasar sun shaidawa Sashen Hausa na Muryar Amurka cewa suna ta jin karar shawagin jiragen yakin sojan kasar da kuma karar manyan bidigogi anata harbe harbe.

Sannan mazauna garin sun yi kira ga gwamnati da ta rinka daukan matakai akan wadannan miyagu kafin su kawo hari a cikin garuruwan su.

Wata majiya mai tushe daga rundunar sojan Najeriya ta tabbatarwa Sashen Hausa na Muryar Amurka cewa mayakan kungiyar Boko Haram sun yi yunkurin kai hari, amma rundunar sojan ta dakile shi.

Wani masanin tsaro ya ce a jihar Yobe ne wannan ta’addanci na kungiyar Boko Haram ya fara kafin ya bazu zuwa jihar Borno, wanda ya watsu zuwa wasu sauran garuruwa.

Ya kuma bukaci dakarun tsaron Najeriya da su nunawa duniya cewa suna aiki tukuru wajan magance wannan matsalar data ki ci taki cinyewa.

More News

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban RiÆ™on Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...