Wani ginin bene ya ruguzo a yankin Bode dake Ibadan babban birnin jihar Oyo.
Wata majiya dake yankin ta shedawa jaridar The Cable cewa lamarin yafaru ne da misalin karfe 05:50 na yamma.
Ruftawar ginin na zuwa ne kasa da sa’o’i 48 bayan ruftawar wani ginin bene dake dauke da makarantar firamare a yankin Itafaji a jihar Lagos inda akalla mutane 20 suka rasa rayukansu.
Ana tsammanin cewa mutane da dama sun makale a cikin ginin benen.
Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar Oyo,ya tabbatarwa da kamfanin Dillancin Labaran Najeriya cewa ana cigaba da aikin ceto a wurin da lamarin yafaru.
“Abin da yafi muhimmanci a yanzu shine kawar da baraguzan ginin, domin ceto mutanen da suka makale bayannan kuma sai tantance wadanda abin ya rutsa da su,”ya ce.