Belgium ta ci gaba da zama ta daya a fagen tamaula a duniya | BBC Hausa

Belgium National team

Tawagar kwallon kafa ta Belgium ta ci gaba da zama ta daya a jerin wadanda ke kan gaba a fagen taka leda a jadawalin da Fifa ta fitar ranar Alhamis.

Mali da Morocco suna daga cikin wadanda suka yi sama a jerin wadanda suka yi fice a kwallon kafa da hukumar kwallon kafa ta duniya, Fifa ta bayyana.

Tawagar Belgium da ta Faransa da Brazil da Ingila da kuma Portugal sun ci gaba da zama a sawun yan gaba-gaba.

Sauran da ke cikin ‘yan 10 farko sun hada da tawagar Spaniya da ta Argentina da Uruguay da Mexico da kuma Italiya, yayin da Jamus ke mataki na 13.

Morocco tana ta 33 a duniya wadda ta taka mataki biyu, bayan da ta lashe Chan a bana, Mali wadda ta yi ta biyu a gasar tana ta 54 a duniya.

Tawagar Uganda da ta Zimbabwe sun ci karo da koma baya zuwa kasa da gubi hudu.

Ranar 8 ga watan Afirilu hukumar kwallon kafa ta duniya Fifa za ta fitar da jerin wadanda ke kan gaba a kwallon kafa a duniya na gaba.

Wadanda ke kan gaba a taka leda a Afirka:

  • Senegal
  • Tunisia
  • Algeria
  • Morocco
  • Najeriya
  • Masar
  • Kamaru
  • Ghana
  • Mali
  • Burkina Faso

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...