Bayern Munich: Ban tattauna da kowa ba – Wenger

Arsene Wenger

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Wenger ya lashe Premier sau uku a Arsenal cikin shekara 22

Arsene Wenger ya musanta rahotannin da ke cewa zai karbi aikin horar da Bayern Munich.

Sai dai tsohon mai horar da Arsenal din bai nisanta kansa daga aikin ba.

Zakarun Bundesliga, Munich na neman sabon mai horarwa bayan sun kori Niko Kovac a ranar Lahadi biyo bayan kwallo biyar da kungiyar Frankfurt ta dura masu.

Wenger ya lashe kofin Premier sau uku a Arsenal a shekara 22 da ya shafe a kulob din kafin ya ajiye aiki a karshen kakar 2017-2018.

  • An tambayi dan shekara 70 din lokacin da yake yin sharhi a tashar talabijin ta beIN Sports a ranar Laraba game rade-radin. Sai ya ce:

    “Ban taba daina magana da su ba saboda na san jagororin kulob din sama da shekara 30.

    “Na kusa koma wa Bayern a shekarun baya. A yanzu dai ban yi magana da kowa ba. Mun dai yi magana a baya amma ban sani ba ko za mu sake yi.

    Bayern Munich tana mataki na hudu a teburin Bundesliga, maki hudu tsakaninta da Borussia Mönchengladbach wadda ke saman teburi.

    More News

    EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

    Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

    Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

    Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

    Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

    Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

    Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

    A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...