Bauchi: INEC Ta Soke Zaben Karamar Hukumar Tafawa Balewa

Labarin da ke fitowa da duminta daga cikin ofishin INEC da ke Bauchi, na tabbatar da cewar babban jami’in tattara sakamakon zaven gwamnan jihar Bauchi Farfesa Kyary Muhammad mukaddashin shugaban jami’ar Futi da ke Yola, ya soke zaben karamar hukumar Tafawa Balewa da ke jihar ta Bauchi.

Farfesan ya soke sakamakon zaben ne bayan da muhawara mai karfi ta barke a tsakanin wakilan jam’iyyun da suka hada da APC, PDP, PRP, jimkadan bayan da jami’ar tattara sakamakon wannan mazabar ta bayyana kalubalen da suka fuskanta a lokacin gudanar da zaben da lokacin tattara sakamakon zaben.

Misis Dominion Anosike ita ce jami’ar tattara sakamakon zaben mazabar karamar hukumar Tafawa Balewa, ta shaida a filin amsar sakamakon cewar an tursasa mata wajen shigar da ababen da basu dace ba a yayin da ake tattara sakamakon zaben wannan karamar hukumar.

Tana mai shaida cewar an samu barazana sosai da kuma fuskantar mummunar kalubale na kai mata farkamaki, inda ta shaida cewar hatta sakamakon zaben da ta zo da shi, ta zo da shi ne ba a takardar da ya dace a kawo sakamakon zaben ba, ta ce, hakan ya faru ne kuma a sakamakon farmakin da aka kai mata, don haka ne ta ce sakamakonta akwai matsala a ciki.

Jami’in jam’iyyar APC a wajen, ya shaida cewar sakamakon zaben na bogi ne wanda aka tsara a gefe, don haka ne ya buqaci shugaban da ke amsar sakamakon zaben ya yi nazarin sakamakon cikin hanzari.

Wakilin jam’iyyar PDP shi kansa bai yi musun matsala ba, inda ma ya ce a dokance yake idan da an samu artabu da kai farmaki a wajen rumfunar zabe har aka tabbatar da fada shine za a soke zaben, ya dai nemi kada a soke zaben karamar hukumar gaba daya, ya ce amma muddin har aka zo wajen bayar da sakamakon zabe ba tare da matsala ba shi kenan.

Nan take dai shugaban da ke tattara sakamakon zaben ya sanar da soke zaben a bisa rashin sahihancin zaben.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...