[ad_1]
Ćłansanda uku aka rawaito an kashe akan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna lokacin da wasu barayi suka kai musu harin kwanton bauna.
Barayin sun kuma kona motar da ƴansandan suke gudanar da sintiri a ciki lokacin da aka kai musu harin acewar ƙungiyar Birnin-Gwari Vanguards for Security and Good Governance.
Kungiyar ta ce lamarin yafaru ne kusa da kauyen Labi dake karamar hukumar ta Birnin Gwari.
A cikin wata sanarwa, Ibrahim Nagwari, shugaban kungiyar ya mika sakon ta’aziyar kungiyar ga iyalan ƴansandan da lamarin ya rutsa da su.
Shugaban kungiyar ya kuma yabawa namijin ƙoƙarin da jami’an tsaro suke na samar da tsaro a yankin.
Ya zuwa yanzu dai rundunar Ć´ansandan jihar Kaduna ba tace komai ba akan faruwar lamarin.
[ad_2]