Bakin Haure 83 Daga Nahiyar Afirka Sun Mutu a Teku | BBC Hausa

Jirgin ya nutse ne a tekun Meditaraniya kwanaki biyu da suka gabata, ‘yan sa’o’i bayan da suka taso daga garin Zuwara na kasar Libya.

Wani masunci ne ya gano mutane hudu kan wasu katakai akan ruwa, ya kuma shaida wa hukumomi. ‘daya daga cikin mutane hudun da suka tsira daga bisani ya rasu a asibiti. Kungiyar agaji ta Red Cross ta ce jirgin yana dauke da mutane masu yawan gaske ne.

‘Daya daga cikin wadanda suka tsira ya ce ruwa ne ya fara cin jirgin yayin da bakin hauren suke iya ganin haske a bakin gabar ruwa. Kiran waya na gaggawa domin neman taimako bai sami nasara ba, saboda wanda ya kira ya kasa fadawa ma’aikatan ceto inda jirgin nasu ya ke.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...