Bakin Haure 83 Daga Nahiyar Afirka Sun Mutu a Teku | BBC Hausa

Jirgin ya nutse ne a tekun Meditaraniya kwanaki biyu da suka gabata, ‘yan sa’o’i bayan da suka taso daga garin Zuwara na kasar Libya.

Wani masunci ne ya gano mutane hudu kan wasu katakai akan ruwa, ya kuma shaida wa hukumomi. ‘daya daga cikin mutane hudun da suka tsira daga bisani ya rasu a asibiti. Kungiyar agaji ta Red Cross ta ce jirgin yana dauke da mutane masu yawan gaske ne.

‘Daya daga cikin wadanda suka tsira ya ce ruwa ne ya fara cin jirgin yayin da bakin hauren suke iya ganin haske a bakin gabar ruwa. Kiran waya na gaggawa domin neman taimako bai sami nasara ba, saboda wanda ya kira ya kasa fadawa ma’aikatan ceto inda jirgin nasu ya ke.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]