Babban limamin Suleja ya rasu awanni bayan dawowa daga Saudiyya

Limamin babban masallacin Juma’a na garin Suleja dake jihar Niger, Sheikh Dahiru Shuaibu ya mutu ranar Asabar awanni kadan bayan ya dawo daga aikin Hajji a kasar Saudiya.

Abduljalil Dahiru Daya daga cikin iyalan , mamacin ya ce limamin wanda ya dawo daga Saudiyya a ranar Asabar wajen karfe 09:00 na safe ya mutu sanadiyar bugawar zuciya da misalin karfe 11:00 na dare a gidansa

Ya ce “Ina daya daga cikin iyalan da suka je filin jirgin saman Abuja da safiyar ranar Asabar domin tarbar liman. Amma da wajen karfe 11:00 na dare sai aka kira ni a cewar liman ya rasu.”

Tuni aka yi Jana’izar marigayin inda aka binne gawarsa kamar yadda addinin musulunci ya tanada a makabartar musulmai dake Suleja

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...