Babban limamin Suleja ya rasu awanni bayan dawowa daga Saudiyya

Limamin babban masallacin Juma’a na garin Suleja dake jihar Niger, Sheikh Dahiru Shuaibu ya mutu ranar Asabar awanni kadan bayan ya dawo daga aikin Hajji a kasar Saudiya.

Abduljalil Dahiru Daya daga cikin iyalan , mamacin ya ce limamin wanda ya dawo daga Saudiyya a ranar Asabar wajen karfe 09:00 na safe ya mutu sanadiyar bugawar zuciya da misalin karfe 11:00 na dare a gidansa

Ya ce “Ina daya daga cikin iyalan da suka je filin jirgin saman Abuja da safiyar ranar Asabar domin tarbar liman. Amma da wajen karfe 11:00 na dare sai aka kira ni a cewar liman ya rasu.”

Tuni aka yi Jana’izar marigayin inda aka binne gawarsa kamar yadda addinin musulunci ya tanada a makabartar musulmai dake Suleja

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]