Babban limamin Suleja ya rasu awanni bayan dawowa daga Saudiyya

Limamin babban masallacin Juma’a na garin Suleja dake jihar Niger, Sheikh Dahiru Shuaibu ya mutu ranar Asabar awanni kadan bayan ya dawo daga aikin Hajji a kasar Saudiya.

Abduljalil Dahiru Daya daga cikin iyalan , mamacin ya ce limamin wanda ya dawo daga Saudiyya a ranar Asabar wajen karfe 09:00 na safe ya mutu sanadiyar bugawar zuciya da misalin karfe 11:00 na dare a gidansa

Ya ce “Ina daya daga cikin iyalan da suka je filin jirgin saman Abuja da safiyar ranar Asabar domin tarbar liman. Amma da wajen karfe 11:00 na dare sai aka kira ni a cewar liman ya rasu.”

Tuni aka yi Jana’izar marigayin inda aka binne gawarsa kamar yadda addinin musulunci ya tanada a makabartar musulmai dake Suleja

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]