Ba zan goyi bayan Buhari kan ta-zarce ba—Shekarau

Shekarau

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Tsohon gwamnan Kano, Ibrahim Shekarau, ya ce ba zai goyi bayan shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ba idan ya nemi karin wa’adi karo a uku.

Shugaba Buhari dai ya sha musanta zargin da wasu ‘yan kasar, musamman ‘yan jam’iyyar hamayya ta PDP, ke yi cewa yana so a yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima domin ya ci gaba da mulki kar na uku.

Sai dai a tattaunawarsa da BBC kan kudurin da majalisar dattawan kasar ta amince da shi na bukatar gyaa ga kundin tsarin mulkin kasar, Sanaa Shekarau ya ce ba ya tsammanin Shugaba Buhari zai nemi yin ta-zarce saboda kaunarsa ga mulkin dimokradiyya.

“Ni dai a iya sanina ban san asalin wannan magana [yunkurin ta-zarcen Buhari ba]; idan ma akwai ta ni ban ji ta ba, ba a yi da ni ba…ko da irin wannan batu zai zo ina daga cikin sahun gaba da za su ce basu yarda ba.”

  • ‘Buhari ba zai sauya tsarin mulki don neman tazarce ba’

Tsohon gwamnan na Kano ya bukaci ‘yan kasar su kyautatawa Shugaba Buhari zato, yana mai cewa “yadda nake kyautata wa Janar Buhari zato ko da mafi kusancinsa sun kawo masa irin wannan tunani, ga hange na ba najin zai karbi wannan tsaro.”

A cewarsa, idan Buhari ya nemi yin ta-zarce hakan zai haifar da fitina a kasar.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Buhari ya ce ba zai nemi yin ta-zarce ba

More News

Kotu ta bayar da belin Hadi Sirika da Ć´arsa

Wata babbar kotun tarayya dake Abuja ta bayar da belin tsohon ministan harkokin sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da kuma wasu mutane uku kan...

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban RiĆ™on Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...