Rahotanni sun tabbatar da cewa Ministan Sadarwa, Adebayo Shittu,bai halarci shirin yi wa kasa hidima (NYSC) bayan ya kammala karatun digiri a jami’ar Obafemi Awolowo da ke Ife a lokacin yana da shekaru 25 da haihuwa.
A bisa dokar kasa, duk wanda ya kammala digiri kuma bai wuce shekaru 30, dole ya halarci shirin NYSC kuma kin yin hakan Babban laifi ne wanda hukuncinsa ya kai zaman gidan kurkuku na tsawon shekaru 14. Irin wannan laifin ne ya tilastawa Ministar Kudi, Kemi Adeosun yin murabus
.