Al’ummomi musamman a arewacin Nijeriya na ci gaba da murna da mayar da martani tun bayan sanarwar da kamfanin samar da man fetur na kasar NNPC ya bayar cewa an gano man fetur da iskar gas a kogin Kolmani.
A farkon watan Fabrairun bana, Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da aikin fara tonon rijiyoyin mai a yankin da ya hada da jihar Bauchi da Gombe da Yobe gami da Adamawa.
Wata sanarwa da kamfanin NNPC ya fitar a karshen mako ta ce suna ci gaba da aiki a Kogin Kolmani don tabbatar da ko yawan man fetur d’in ya kai adadin da za a iya cinikayyarsa.
An shafe tsawon shekaru, ana fafutukar ganin hako man din da ake cewa akwai shi jibge a wasu sassan arewa maso gabashin Najeriya.
- An samu man fetur a Bauchi – NNPC
- ‘Barayin fetur na sa kamfanin Shell asarar $560,000 kullum a Najeriya’
Sanata Salisu Ibrahim Musa Matori na daya daga cikin dattijan jihar Bauchi, wadanda suka dade suna ta fadi-tashin ganin cikar wannan buri, kuma ya shaidawa BBC cewa sama da shekaru 20 da suka gabata aka fara batun,
”To amma gwamnatin wancan lokacin ba ta maida hankali akai ba, watakil saboda ba ya cikin ajandarta. Sai bayan zuwan wannan gwamnati na APC ne aka sake matsa kai mi kuma Allah cikin ikonsa ta tabbata akwai mai a kogin Kolmani”, inji Matori.
Matori ya kara da cewa” Alfanun da za a ci na samun mai da iskar gas zai kasance ya raba matasa da zaman kashe wando, da samawa gwamnati kudaden shiga wanda muke fatan Najeriya baki daya za ta amfana da shi”.